fidelitybank

Gwamnan Kano ya gwangwaje zakarun gasar karatun Alkur’ani da kujerar Hajji da miliyoyin Naira

Date:

An gudanar da taron karshe na gasar a makarantar nazarin harsunan Larabci (School of Arabic Studies), Kano, inda Buhari Sunusi Gezawa da Fatima Abubakar Tarauni suka fito a matsayin zakarun gasar na bangaren maza da mata, bi da bi.

Da yake wakiltar Gwamna Yusuf, Mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya yabawa dukkan mahalarta gasar kan jajircewarsu da hazakarsu a tsawon lokacin gasar.

Ya bayyana fatansa cewa wakilan Kano za su yi fice a gasar karatun Al-Qur’ani ta kasa mai zuwa, wadda za a gudanar a wannan watan a Jihar Kebbi.

Gwamnan ya jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da inganta ilimin addini, tallafa wa makarantun Islamiya, da kuma karfafa tsarin Tsangaya.

Haka kuma, ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su ci gaba da yin addu’a domin samun mafita ga matsalolin tsaro a Najeriya da kuma zaman lafiya a kasashen Musulmi da ke fama da rikice-rikice, irin su Sudan, Falasdinu, da Siriya.

A nasa jawabin, Sarkin Kano, Dakta Muhammad Sunusi II, ya taya wadanda suka yi nasara murna tare da yabawa matsayin Kano a matsayin gari mai daraja ga Al-Qur’ani da Manzon Allah (SAW).

Ya danganta zaman lafiya da ake morewa a Kano da wadannan kyawawan dabi’u da aka taru a kai, sannan ya yaba wa kokarin gwamnati na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya tsakanin addinai.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp