fidelitybank

Gwamnan Kano ya gwangwaje zakarun gasar karatun Alkur’ani da kujerar Hajji da miliyoyin Naira

Date:

An gudanar da taron karshe na gasar a makarantar nazarin harsunan Larabci (School of Arabic Studies), Kano, inda Buhari Sunusi Gezawa da Fatima Abubakar Tarauni suka fito a matsayin zakarun gasar na bangaren maza da mata, bi da bi.

Da yake wakiltar Gwamna Yusuf, Mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya yabawa dukkan mahalarta gasar kan jajircewarsu da hazakarsu a tsawon lokacin gasar.

Ya bayyana fatansa cewa wakilan Kano za su yi fice a gasar karatun Al-Qur’ani ta kasa mai zuwa, wadda za a gudanar a wannan watan a Jihar Kebbi.

Gwamnan ya jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da inganta ilimin addini, tallafa wa makarantun Islamiya, da kuma karfafa tsarin Tsangaya.

Haka kuma, ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su ci gaba da yin addu’a domin samun mafita ga matsalolin tsaro a Najeriya da kuma zaman lafiya a kasashen Musulmi da ke fama da rikice-rikice, irin su Sudan, Falasdinu, da Siriya.

A nasa jawabin, Sarkin Kano, Dakta Muhammad Sunusi II, ya taya wadanda suka yi nasara murna tare da yabawa matsayin Kano a matsayin gari mai daraja ga Al-Qur’ani da Manzon Allah (SAW).

Ya danganta zaman lafiya da ake morewa a Kano da wadannan kyawawan dabi’u da aka taru a kai, sannan ya yaba wa kokarin gwamnati na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya tsakanin addinai.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka Æ´an Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar HaÉ—in kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran Æ™asa za ka mayar da kai ba zaÉ“en 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp