An gudanar da taron karshe na gasar a makarantar nazarin harsunan Larabci (School of Arabic Studies), Kano, inda Buhari Sunusi Gezawa da Fatima Abubakar Tarauni suka fito a matsayin zakarun gasar na bangaren maza da mata, bi da bi.
Da yake wakiltar Gwamna Yusuf, Mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya yabawa dukkan mahalarta gasar kan jajircewarsu da hazakarsu a tsawon lokacin gasar.
Ya bayyana fatansa cewa wakilan Kano za su yi fice a gasar karatun Al-Qur’ani ta kasa mai zuwa, wadda za a gudanar a wannan watan a Jihar Kebbi.
Gwamnan ya jaddada kudirin gwamnatinsa na ci gaba da inganta ilimin addini, tallafa wa makarantun Islamiya, da kuma karfafa tsarin Tsangaya.
Haka kuma, ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su ci gaba da yin addu’a domin samun mafita ga matsalolin tsaro a Najeriya da kuma zaman lafiya a kasashen Musulmi da ke fama da rikice-rikice, irin su Sudan, Falasdinu, da Siriya.
A nasa jawabin, Sarkin Kano, Dakta Muhammad Sunusi II, ya taya wadanda suka yi nasara murna tare da yabawa matsayin Kano a matsayin gari mai daraja ga Al-Qur’ani da Manzon Allah (SAW).
Ya danganta zaman lafiya da ake morewa a Kano da wadannan kyawawan dabi’u da aka taru a kai, sannan ya yaba wa kokarin gwamnati na ci gaba da tabbatar da zaman lafiya tsakanin addinai.