fidelitybank

Gwamnan Kano ya damu a kan hukumomin Karota da REMASAB

Date:

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya nuna damuwarsa kan yadda ma’aikatun tsaftar muhalli da ta karota ke gudanar da ayyukansu a jihar.

Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, gwamnan ya yumarci ma’aikatun biyu su gabatar da cikakken bayanan kayayyakin aikinsu domin tabbatar da ingancinsu.

Gwamnan ya bayar da umarnin ne bayan wata ziyarar ba-zata da ya kai hukumomin, inda ya tarar da gazawar ma’aikatun tare da jami’an hukumomin.

Abba Kabir ya nuna damuwarsa kan yadda hukumomin ke gudanar da ayyukansu, duk da irin kuɗin da ya ce gwmnati na zubawa a ma’aikatun”, in ji sanarwar.

A hukumar tsaftar muhalli ta jihar, gwamnan ya tarar da motocin kwashe shara bakwai ne kawai ke aiki daga cikin 30 da hukumar ke da su, kamar yadda ya samu motocin loda wa manyan motoci (felloda) uku ne kawai ke aiki daga cikin 15 da ma’aikatar ke da su.

Sanarwar ta cea lokacin ziyarar an shaida wa gwamnan cewa ma’aikatan dindindin 10 ne kawai hukumar ke da su, yayin da sauran duka na-wucin gadi ne.

Abba Kabir ya kuma nuna damuwarsa kan halin da ma’aikatan wucin gadin suke ciki, wanda ya bayyana da zalunci ne mutum ya yi shekara 20 a matsayin ma’aikacin wucin-gadi.

Haka kuma a ma’aikatar kula da dokokin titi ta Karota, gwamna ya tarar da motoci masu yawa da suka lalace.

Inda ya buƙaci hukumar ta gaggauta kai masa cikakken rahoton motocin da ma’aikatar ke da su

Abba Kabir ya ce yadda gwamnati ke zuba makudan kuɗi a hukumar tsaftar muhallin a nuna irin muradin da gwamnati ke da shi wajen tabbatar da tsaftar muhalli, to amma ya ce hukumar ta gaza yin abin da ya dace.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp