Gwamnan jihar Lagos ya rushe majalisar zartarwarsa kafin rantsar da shi da za a sake yi a ranar Litinin 29 ga watan Mayu, 2023.
Za a rantsar da Sanwo-Olu da mataimakinsa Obafemi Hamzat, a karo na biyu na wa’adin shekara hudu a ranar Litinin din.
Shugaban ma’aikatan jihar Hakeem Muri-Okunola, shi ne ya bayar da sanarwar a yau Laraba ta wata takardar da ta fito daga ofishinsa.
Takardar tana dauke da bayanin da ke nuna sauke masu rike da ofisoshi na siyasa wato kwamishinoni da ma wadanda ba kwamishinoni ba.