fidelitybank

Gwamnan Jigawa ya tallafawa Maniyata Naira miliyan 1 cikon kudin Hajji

Date:

Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya amince da Naira miliyan 1 a matsayin tallafi ga kowane mahajjatan jihar da za su yi aikin Hajjin shekarar 2024.

Babban Daraktan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da manema labarai a Dutse babban birnin jihar.

Hakan ya biyo bayan karin farashin kudin da hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta yi a baya bayan nan, sakamakon yadda farashin canji ya samu karbuwa.

Wannan dai na zuwa ne kwanaki bayan da jaridar DAILY POST ta ruwaito cewa, fitaccen malamin addinin musuluncin nan, Sheikh Kabiru Gombe, ya bukaci gwamnatin Najeriya da gwamnonin jihohin kasar da su kai dauki ga maniyyata.

Labbo ya bukaci maniyyatan jihar da su tabbatar sun mika sauran kudaden da suka rage na sama da N918,000 ga hukumar.

Ya yi nuni da cewa wadanda za su ci gajiyar tallafin aikin Hajji su ne wadanda tuni suka biya wani bangare na kudaden da hukumar jin dadin alhazai ta jihar ta yi.

Hukumar NAHCON ta sanar da karin kudin aikin Hajji da N1,918,032.91, wanda ya kai adadin zuwa N6,617,032.91.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp