Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya, ya gabatar da jawabi a cibiyar kula da harkokin kasashen waje ta Birtanya kan batun inganta kiwon lafiya.
An gayyace shi ne musamman domin baje kolin irin nasarar da ya samu a gwamnatinsa wurin tallafa wa ɓangaren kiwon lafiya.
Gwamnan Legas Babajide Sanwo-Olu da kuma Abdullahi Sule na Nasarawa na daga cikin wadanda suka halarci taron.
Gwamna Yahaya ya bayyana cewa an gyara asibitocin ƙwararru da kuma cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko a faɗin mazabu 114 da kuma aikin da ake yi na gyara babban asibitin jihar.