fidelitybank

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Date:

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami’an sojojin ƙasar da sakaci wajen rashin kama maharan da suka kashe mutum 27 a garin Tahoss na yankin ƙaramar hukumar Riyom.

A farkon makon nan ne wasu mahara ɗauke da makamai suka auka wa garin tare da halaka mutum 27 da raunata wasu.

Yayin wata hira da gidan talbijin na Channels ranar Juma’a ta cikin shirin ”The Morning Brief” kwamishiniyar yaɗa labaran jihar, Joyce Ramnap ta ce sojojin da ke yankin sun nuna sakaci wajen rashin kama ko da mutum guda cikin maharan, duk kuwa da kasancewar sojojin a kusa da garin.

Kwamishiniyar ta ce garin da aka kai harin na kusa da shingen binciken ababen hawa da sojoji ke gudanarwa.

“Akwai shingen binciken ababen hawa na sojoji, wanda bai fi tazarar mita 200 daga wurin da lamarin ya faru, kuma daga bayanan da muka samu ba wanda suka kama, kuma ba su kashe kowa ba”.

“Garin nan ba wani gari ba ne mai nisa da za a ce kafin a kai inda suke an yi musu lahani, suna kusa da titi,” in ji ta.

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp