Gwamnan jihar Edo, Sanata Monday Okpebholo, ya yi Alla-wadai da kashe wasu matafiya da aka yi a garin Uromi da ke ƙaramar hukumar arewa maso gabashin Esan a ranar Alhamis da ta gabata, wato 27 ga Maris, inda ya bayyana kisan da na dabbanci.
Ana ta dai yaɗa wasu faya-fayan bidiyo, wanda a ciki aka nuna wasu matasa sun zagaye wasu mutane da ake tunanin mafarauta ne ƴan arewa da suka taso daga kudancin ƙasar za su koma gida wataƙila domin bikin sallah.
A wata sanarwa da sakataren watsa labaran gwamnan jihar, Fred Itua ya fitar, ya ce, “Binciken farko-farko ya nuna cewa matafiya ne da suka taso daga Fatakwal na jihar Rivers suka ratso ta garin, sai ƴan banga suka kama su da tunanin cewa ɓatagri ne.”