Gwamnan Ebonyi Dave Umahi ya sanar da shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, aniyarsa ta neman kujerar shugaban kasa a ƙarƙashin jam’iyyar APC.
Ƙasa da awanni 24 bayan da jagoran jam’iyyar APC a Najeriya, Bola Tinubu ya sanar da shugaba Muhamamdu Buhari zai yi takarar shugaban ƙasa.
Umahi ya bayyana hakan ne ga manema labaran fadar shugaban ƙasa bayan ganawa da shugaba Muhammadu Buhari.
Bayan su akwai ƙarin wasu mutane da suma ake raɗe-raɗin za su bayyana aniyarsu nan ba da jimawa ba.