Dan takarar gwamnan jihar Ebonyi na jam’iyyar PDP, Iduma Igariwey, ya bukaci gwamna David Umahi da ya gaggauta barin ofis tare da mataimakinsa.
Jam’iyyar PDP ta tsayar da Mista Igariwey ne biyo bayan hukuncin da kotun tarayya da ke Abuja ta yanke a ranar 8 ga watan Maris, inda ta kori Mista Umahi da mataimakinsa, saboda sauya sheka daga PDP zuwa jam’iyyar APC.
Igariwey ya yi wannan kiran ne ranar Alhamis a Abuja yayin da yake mayar da martani kan hukuncin da kotun ta yanke.
Jam’iyyar PDP ta mika sunan Mista Igariwey da na mataimakinsa, Fred Udogu ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC a matsayin wanda zai maye gurbin Mista Umahi da mataimakinsa, bisa bin umarnin kotu.