Gwamnan jihar Bauchi kuma dan takarar kujerar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Bala Mohammed, ya gana da tsaffin ministocin jam’iyyar PDP, kwamitin ayyuka na kasa, NWC da kuma mambobin kwamitin amintattu na jam’iyyar, domin neman goyon bayansu a yunkurinsa na neman tikitin shugaban kasa a jam’iyyar.
Mohammed, a ganawar da ya yi da tsaffin ministocin a ranar Talata a Transcorp Hilton Abuja, ya ce burinsa na zama shugaban kasa ya biyo bayan bukatar ceto kasar.
Ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya karkashin jam’iyyar APC ta ruguza kasar, yana mai cewa akwai bukatar ja da Najeriya daga kangi.
A cewarsa, “Al’umma ba ta nan kamar yadda muka bar ta ba, sun lalata komai.
“Da farko dole ne mu fahimci kasar. Ina muke kuma yaya muka zo nan? Me yasa kasar ta rabu haka? Me yasa rashin tsaro ya kasance a ko’ina? Menene makomar masu fada aji a kasar nan da muke mambobi dominta?
“Mun san ba za mu iya ci gaba da wasan zargi ba. Ba za mu iya ci gaba da magana game da sassan ko yankuna ba. Dole ne mu yi magana game da shugabanci, rufe matsayi, haɗuwa don ceton ƙasa. Akwai talauci a ko’ina. Akwai rashin tsaro a ko’ina.
“Ko da jarin dan Adam don gudanar da kasa ba son rai ya mamaye komai.”
Gwamnan Bauchi ya yi alkawarin tafiyar da gwamnati mai ilimi, idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa da kuma samar da ingantaccen tsari da zai magance kalubalen da kasar nan ke fuskanta.