Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammed, ya amince da nadin Alhaji Nuhu Ahmed Wabi a matsayin sabon sarkin Jama’are.
Gwamnan ya bayyana amincewarsa ne a wani biki da a ka yi a Jama’are, Bauchi a ranar Litinin, inda sabon sarkin ya karbi takardar kama aiki.
Daily Trust ta rawaito cewa, gwamnan Bauchi ya amince da naÉ—in Nuhu Wabi matsayin sabon sarkin Jama’are. Nadin Nuhu Wabi ya bayyana bayan sati uku da mutuwar mahaifinsa, Alhaji Ahmadu Muhammadu Wabi, wanda ya rasu a ranar 5 ga watan Fabrairu. Ya yi shekaru 52 yana mulki.