Fadar shugaban kasa, ta yi kira ga gwamnan Bauchi, Bala Mohammed ya daina amfani da sukar gwamnatin Tinubu a matsayin hanyar wanke kansa.
A farkon makon nan ne wani bidiyon gwamnan ya ɓulla a shafukan sada zumunta, inda a ciki ya zargi gwamnatin Tinubu da bijiro da wasu manufofi da suka haifar da wahalhalu a ƙasar, musamman batun haraji.
A wata ziyara ta shugaban majalisar malamai ta ƙungiyar Izala, Sheikh Sani Yahaya Jingir, ga gwamnan na jihar Bauchi, Bala Mohammed ya buƙaci Shehin malamin ya faɗa wa Tinubu cewa manufofin gwamnatinsa ba sa aiki.
Cikin wata sanarwa da mataimaki na musamman ga shugaban Ć™asar kan harkokin yaÉ—a labarai, Sunday Dare ya fitar, ya zargi gwamnan da gudanar da “siyasa irin ta jagaliya, maimakon mayar da hankali wajen magance matsalolin da jiharsa ke fuskanta”.
Ya Ć™ara da cewa “burin Shugaba Tinubu shi ne gina Ć™asar ta hanyar haÉ—a kai da gwamnatocin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki.
”Shugaba Tinubu mutum ne mai sauraron jama’a, wanda ya aminta da gwamnatocin jihohi,” in ji shi.
Dangane da batun ƙudirin haraji kuwa, Sunday Dare ya ce shugaban ya bayyana ƙarara cewa duk wanda ke da magana kan ƙudirin to yana gaban majalisar dokokin ƙasar.
”Kuma yin fatali ko sukar wannan tsari ya saÉ“a wa dimokraÉ—É—iya”, in ji shi.
A saboda haka ne Sunday Dare ya buĆ™aci gwamnan na jihar Bauchi ya sauke nauyin da ke kansa na al’ummar jiharsa, maimakon tsayawa sukar gwamnatin Tinubu.
”Surutu da ihu da siyasar jagaliya ba za ta bari ya sauke nauyin mutanen Bauchi da ke wuyansa ba”.
Tun bayan ɓullo da batun harajin, gwamnan na Bauchi na daga cikin gwamnonin arewacin ƙasar da suka riƙa suka a kansa, saboda zargin zai cutar da yankin.