Tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi, ya tabbatar da cewa, ba za a cire rubutun Larabci a cikin kudin Naira daga cikin kudin da aka sake fasalin ba.
Sanusi ya yi ikirarin cewa Babban Bankin Najeriya, CBN, Gwamna Godwin Emefiele ya ba shi tabbacin ba za a cire rubutun Larabci ba daga cikin takardun da aka sake fasalin.
A makon da ya gabata ne CBN ya bayyana cewa ya sake fasalin takardun kudi na N100, N200, da N1000, wanda zai fara aiki a ranar 5 ga Disamba, 2022.
Ra’ayoyi mabanbanta sun yi maraba da sanarwar CBN yayin da wasu malaman addinin Musulunci suka yi zargin cewa sake fasalin Naira wani shiri ne na cire rubutun Musulunci.
A yayin da malaman addinin Islama ke zargin wasu ‘yan Najeriya sun bukaci babban bankin kasar da ya cire rubutun daga cikin kudin da aka sake fasalin na naira.
Da yake mayar da martani, Sanusi ya bukaci shugabannin addinin Musulunci da su tantance bayanansu tare da dakatar da ikirarin da ba su da tushe.
“An yi ta cece-kuce game da sauya wasu takardun kudin Naira. Na ji malamai daban-daban suna sharhi, wasu na nuni da cewa za a cire Ajami a kan kudin Naira.
“Tun da batun ya taso, mun tattauna da wasu mutane a babban bankin kasar, kuma sun tabbatar min da cewa babu irin wannan shiri.
“Lokacin da wannan mummunar fahimta ta yadu, na yi magana da Gwamnan CBN da kansa, kuma ya tabbatar min da cewa babu wani shiri ko kadan na tsige Ajami.
“Don haka, ina so in yi kira ga malaman addinin Musulunci da su daina aiki da rahotannin da ba su da tushe,” kamar yadda ya shaida wa Daily Nigerian.