Majalisar dattawa, ta ce, za ta gayyaci gwamnan babban bankin kasar Godwin Emefiele,
Domin ya yi mata bayani game da faduwar darajar kudin kasar, abin da ya kara jefa ‘yan kasar cikin matsin tattalin arziki.
Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito cewa sanatocin sun bayyana damuwarsu kan yadda yanzu ake chanza dala daya a kan kusan naira 700,
Suna masu cewa abin bakin ciki ne, kuma abu ne da yake bukatar daukar mataki cikin gaggawa.