Lauyoyin Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, sun ce ma’aikacin bankin na burin zama shugaban Najeriya da kuma shiga a matsayin dan takara a zaben shugaban kasa na 2023.
Lauyan, Maliki Sylvanus, ya bayyana hakan a cikin wata takardar shaidar goyon bayan sammacin da Emefiele ya gabatar a gaban wata babbar kotun tarayya da ke Abuja mai lamba FHC/ABJ/CS/610/2022.
Wannan ya sabawa ikirarin Emefiele a ranar Juma’a cewa har yanzu yana jiran Allah ya dauki mataki kan lamarin.
A cikin takardar rantsuwar mai shafi hudu, Sylvanus, babban lauya a Mike Ozekhome’s Chambers, ya rubuta, Cewa bayanan da aka bayar na cikin sani na sai dai kamar yadda aka bayyana, kuma mai shigar da kara, Mista Godwin Emefiele ya sanar da shi yadda ya kamata.