fidelitybank

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Date:

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta raɗe-raɗen da ake yi cewa yana shirin sauya sheƙa zuwa jam’iyyar haɗaka ta ADC.

Wata sanarwa da gwamna Zulum ya fitar a shafinsa na X, ya ce wasu mutane ne kawai suka kirkiro da labarin don cimma wata manufa.

Zulum ya ce har yanzu yana nan daram cikin jam’iyyar APC.

“Mun samu labarin da ake yaɗa wa a kafafen sada zumunta cewa ina shirin komawa ADC tare da wasu gwamnoni biyar. Wannan labari ba shi da gaskiya, wasu ne kawai suka kirkiro shi domin janyo ruɗani.

“Har yanzu APC nake goya wa baya, da kuma ganin cigaban jihar Borno,” in ji Zulum.

Don haka gwamnan ya buƙaci al’ummar jihar da su yi watsi da labarin.

A ranar Laraba ne manyan ƴan adawar siyasa na Najeriya suka tabbatar da amincewa da jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a matsayin wadda za su yi aiki da ita domin tunkarar zaɓen 2027.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamna Zulum ya musanta shirin sauya sheƙa zuwa ADC

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno ya musanta...

Tinubu ta ceci Najeriya faɗa wa cikin mawuyacin hali – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro, Malam...

Isra’ila za ta aika tawaga Qatar don tattaunawa da Hamas

Isra’ila ta yanke shawarar aika wata tawaga zuwa Qatar...

Jagoran Iran ya bayyana gaban jama’a karon farko tun soma yaƙi da Isra’ila

Jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya bayyana...

Muna aiki tukuru don bunƙasa noma a Najeriya – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya tabbatar da cewa...

Duk wanda ya yi sata idan na zama shugaban ƙasa sai na yake shi – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi alwashin...

Ina nan a PDP na ban gudu ba – Adeleke

Gwamnan jihar Osun, ya musanta rahotonnin da ke cewa...

Tinubu ya isa birnin Rio na Brazil don halartar taron BRICS

Shugaban kasa Bola Tinubu ya isa birnin Rio de...

Matakan da muke ɗauka kan kisan matafiya a Plateau – Mutfwang

Gwamna Caleb Mutfwang na jihar Filato, ya ce gwamnatinsa...

Tinubu ya gaji tattalin arziki da ya kusa durkushewa – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyeson Wike, ya ce...

Har yanzu PDP tana nan da ƙarfinta – Isa Ashiru

Yayin da fagen siyasar Najeriya ke ci gaba da...

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...
X whatsapp