fidelitybank

Gwamna Zulum ya ƙaddamar da aikin raba tallafi ga mutum miliyan biyu

Date:

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya ƙaddamar da aikin raba tallafi ga mutane fiye da miliyan biyu da ambaliyar Maiduguri ta shafa.

Magidanta 5,235 ne a yankin Gwange 1 suka fara amfana da tallafin da gwamnan ya ƙaddamar ranar Talata.

Gwamnan ya ce gidajen mutum 587 da suka amfana daga tallafin sun rushe baki ɗaya inda magidanta 2,365 kuma gidajensu suka samu ƴar matsala sannan mutum 2,283 kuma nasu gidajen sun ɗan taɓu.

Gwamnan ya ce tallafin zai kasance hawa-hawa, inda waɗanda suka samu ƴar matsala a gidajen nasu za su samu naira dubu 100 da ƙaramin buhun shinkafa da wake da tabarmi da barguna da gidan sauro.

Sauran kuma waɗanda ambaliyar ko dai ta rushe musu gida baki ɗaya ko kuma ta illata shi za su karɓi abin da ya dace asarar da suka yi.

Farfesa Zulum ya kuma kara sanar da jama’a cewa yawan kuɗin tallafin da suka samu daga gwamnatoci da ɗaidaikuwar al’umma sun kai naira biliyan 7.5 ya zuwa lokacin ƙaddamar da rabon tallafin ranar Talata.

A ranar Litinin ne dai gwamnan ya ƙaddamar da kwamitin mutum 32 da zai ɗauki alhakn yin rabon tallafin ga al’ummar da ambaliyar ta shafa, inda a lokacin ya sanar da cewa an yi wa al’ummar alƙawarin gudunmowa da ta kai yawan naira biliyan 13,195,500,000.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp