Gwamnan jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo ya ziyarci shelkwatar karamar hukumar Aguata da ke Ekwulobia, inda aka kai harin bam.
A ranar Alhamis din da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga suka yi wa sakatariyar wuta da suka hada da shaguna da ababen hawa da aka ajiye a harabar.
Sai dai Soludo wanda ya duba shelkwatar karamar hukumar da aka kona, ya ce, harin ramuwar gayya ce kawai daga wasu miyagu, wadanda a ranar ne jami’an tsaro suka mamaye sansanonin su, kuma aka kama akasarin su.
Soludo ya ce: “A jiya (Alhamis) jami’an tsaro sun bankado wasu sansanoni masu aikata laifuka a Ogboji da Aguluezechukwu, kuma ramuwar gayya shi ne kona shelkwatar karamar hukumar Aguata da wasu ‘yan ta’addan suka gudu suka yi.