Gwamnatin jihar Osun ta yi gagarumin namijin kokari na raba Garin Kwaki a wani shiri na tallafin abinci mai suna ‘Food Support Scheme’ .
Sabon tsarin zai rage radadin annobar COVID-19 da kuma zaburar da tattalin arzikin yankin.
A na sa ran hakan zai karfafawa matasa wajen rungumar noma ta yadda mutane za su samu abin yi.
Jaridar PM News ta bayyana cewa, a ranar Litinin, 21 ga watan Fubrairu 2022, gwamnatin jihar Osun ta raba gari ga masu karamin karfi. Wanda gwamna Gboyega Oyetola ya raba kilo biyar na garin rogo ga mutane 30, 000 a Osun.