fidelitybank

Gwamna ya fashe da kuka a taron jana’izar harin Cocin Ondo

Date:

An fashe da hawaye a wajen jana’izar wadanda harin ta’addancin da aka kai a cocin Saint Francis Catholic Church a garin Owaluwa a jihar Ondo a ranar 5 ga watan Yuni.

Gwamnan jihar, Rotimi Akeredolu (SAN) ya kasa boye ra’ayinsa a yayin taron da aka gudanar a Mydas Resort and Hotel, Owo, a ranar Juma’a.

Akeredolu, wanda ya yi kuka a lokacin da yake jawabi, ya ce, gwamnati ta kasa kare wadanda harin ta’addancin ya rutsa da su.

Yayin da iyalan wadanda suka rasu da kuma masu juyayin suka yi ta zubar da hawaye, gwamnan ya ce gwamnati ta gaza wajen kare wadanda abin ya shafa da kuma daukacin al’ummar kasar.

A cewar Akeredolu, wanda ya yi ta kuka a duk lokacin da ya ke jawabinsa, ya ce, tsarin gine-ginen tsaron kasar na bukatar gyara. In ji Daily Trust.

Taron ya samu halartar uwargidan gwamnan, Betty, tsohon gwamna Mimiko da sauran manyan baki.

Akeredolu ya ce, “Abin da ya faru da mu a Owo, Jihar Ondo abu ne da ba za a iya misaltuwa ba. Har yanzu na yi imani cewa babu wata kalma da za ta kwatanta abin da ya faru. Muna da mutum 22 da suka rasu a wannan zauren yayin da aka binne wasu daga cikinsu.

“A kidaya na karshe, wadannan dabbobi sun kashe mutane 40. Mun kasa kare mutanen nan. Mun gaza ta fuskar tsaro. Waɗannan rundunan mugunta ba za su yi nasara a kanmu ba.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama ɗan shekara 70 kan zargin kashe ƙanwarsa a Jigawa

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta...

Ahmed Musa za ma sabon shugaban gudanarwar Kano Pillars

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya naɗa kyaftin...

Netherlands da Jamus sun zargi Rasha da aiki da makamai masu guba a Ukraine

Hukumomin leƙen asirin ƙasashen Netherlands da Jamus sun zargi...

Kotu ta bayar da umarni Majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta buƙaci...

Sojoji sun hallaka ƴanbindiga da dama a Plateau

Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ƴanbindiga da dama...

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...
X whatsapp