fidelitybank

Gwamna ya fashe da kuka a taron jana’izar harin Cocin Ondo

Date:

An fashe da hawaye a wajen jana’izar wadanda harin ta’addancin da aka kai a cocin Saint Francis Catholic Church a garin Owaluwa a jihar Ondo a ranar 5 ga watan Yuni.

Gwamnan jihar, Rotimi Akeredolu (SAN) ya kasa boye ra’ayinsa a yayin taron da aka gudanar a Mydas Resort and Hotel, Owo, a ranar Juma’a.

Akeredolu, wanda ya yi kuka a lokacin da yake jawabi, ya ce, gwamnati ta kasa kare wadanda harin ta’addancin ya rutsa da su.

Yayin da iyalan wadanda suka rasu da kuma masu juyayin suka yi ta zubar da hawaye, gwamnan ya ce gwamnati ta gaza wajen kare wadanda abin ya shafa da kuma daukacin al’ummar kasar.

A cewar Akeredolu, wanda ya yi ta kuka a duk lokacin da ya ke jawabinsa, ya ce, tsarin gine-ginen tsaron kasar na bukatar gyara. In ji Daily Trust.

Taron ya samu halartar uwargidan gwamnan, Betty, tsohon gwamna Mimiko da sauran manyan baki.

Akeredolu ya ce, “Abin da ya faru da mu a Owo, Jihar Ondo abu ne da ba za a iya misaltuwa ba. Har yanzu na yi imani cewa babu wata kalma da za ta kwatanta abin da ya faru. Muna da mutum 22 da suka rasu a wannan zauren yayin da aka binne wasu daga cikinsu.

“A kidaya na karshe, wadannan dabbobi sun kashe mutane 40. Mun kasa kare mutanen nan. Mun gaza ta fuskar tsaro. Waɗannan rundunan mugunta ba za su yi nasara a kanmu ba.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp