Gwamnatin jihar Anambra ta cire masu ƙananan sana’o’i da jarinsu yake ƙasa da Naira N100,000 daga biyan haraji.
Kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Law Mefor, ne ya bayyana haka a wata sanarwa a jiya Talata, inda ya ce gwamnatin ta zartar da hakan ne a ƙarshen taron majalisar zartarwar jihar karo na 37, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Mefor ya jaddada cewa har yanzu dokar yaƙi da zaman-banza da kashe wando da yawon tasha ta jihar har yanzu tana nan da ƙarfinta, a don haka ya shawarci matasa su shiga shirin koyar da sana’o’i da bayar da jari na gwamnatin jihar domin cin guminsu ta halaliya.
Kwamishinan ya kuma yi kira ga masu zuba jari da su karɓi kamfanonin gwamnati na jihar, inda yake cewa bayar da su haya ko jinginar da su ga ‘yan kasuwa ya fi a ce gwamnati na tafiyar da su.