fidelitybank

Gwamna Kebbi ya rantsar da sabbin Alkalai tare da siya mu su motocin miliyan 300 kowane

Date:

Gwamnan jiar Kebbi, Dakta Nasir Idris ya rantsar da sabbin alkalan babbar kotun jihar guda hudu da manyan Khadi guda biyu.

Taron rantsuwar ya gudana ne a adar gwamnatin jihar da ke Birnin Kebbi, a ranar Juma’a.

Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Yakubu Bala Tafida, ya gabatar da sunayen sabbin alkalai hudu kamar haka: Mai Girma Hassan Kwaido, Halima Umar Ibrahim, Lauratu Jagwadeji Suru, da Muhammad Nurudeen.

Haka kuma ya gabatar da sunayen Khadi guda biyu da suka hada da Kabiru Aliyu, SAN, da Atiku Muhammad Bello daga kotun shari’a.

A jawabinsa, Gwamna Nasir Idris ya bayyana farin cikinsa tare da taya wadanda aka rantsar murna.

Ya yi alfahari da samun dama ta musamman na rantsar da sabbin jami’an shari’a guda shida.

Gwamnan ya yaba wa Ma’aikatar shari’a ta jihar saboda kokarinta wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyanta, tare da tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da biyan albashi da kula da jin dadin Alkalai a jihar.

“Ina kuma yaba wa Ma’aikatar Shari’a ta Jihar saboda jajircewarta wajen sauke nauyin da ke kanta. Har ila yau, a karkashin wannan gwamnati, ba mu taba samun tangarda daga gare ku ba,” in ji sanarwar Yahaya Sarki, mashawarci na musamman ga Gwamna Nasir Idris.

Haka kuma, Gwamnan ya sanar da amincewarsa da biyan N300m don sayen motocin aiki ga alkalai.

Ya shawarci sabbin jami’an da su yi amfani da kwarewarsu tare da kiyaye ka’idodin aikin shari’a.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp