fidelitybank

Gwamna Kebbi ya rantsar da sabbin Alkalai tare da siya mu su motocin miliyan 300 kowane

Date:

Gwamnan jiar Kebbi, Dakta Nasir Idris ya rantsar da sabbin alkalan babbar kotun jihar guda hudu da manyan Khadi guda biyu.

Taron rantsuwar ya gudana ne a adar gwamnatin jihar da ke Birnin Kebbi, a ranar Juma’a.

Sakataren gwamnatin jihar, Alhaji Yakubu Bala Tafida, ya gabatar da sunayen sabbin alkalai hudu kamar haka: Mai Girma Hassan Kwaido, Halima Umar Ibrahim, Lauratu Jagwadeji Suru, da Muhammad Nurudeen.

Haka kuma ya gabatar da sunayen Khadi guda biyu da suka hada da Kabiru Aliyu, SAN, da Atiku Muhammad Bello daga kotun shari’a.

A jawabinsa, Gwamna Nasir Idris ya bayyana farin cikinsa tare da taya wadanda aka rantsar murna.

Ya yi alfahari da samun dama ta musamman na rantsar da sabbin jami’an shari’a guda shida.

Gwamnan ya yaba wa Ma’aikatar shari’a ta jihar saboda kokarinta wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyanta, tare da tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da biyan albashi da kula da jin dadin Alkalai a jihar.

“Ina kuma yaba wa Ma’aikatar Shari’a ta Jihar saboda jajircewarta wajen sauke nauyin da ke kanta. Har ila yau, a karkashin wannan gwamnati, ba mu taba samun tangarda daga gare ku ba,” in ji sanarwar Yahaya Sarki, mashawarci na musamman ga Gwamna Nasir Idris.

Haka kuma, Gwamnan ya sanar da amincewarsa da biyan N300m don sayen motocin aiki ga alkalai.

Ya shawarci sabbin jami’an da su yi amfani da kwarewarsu tare da kiyaye ka’idodin aikin shari’a.

daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp