Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci wata tawaga daga Gwamnatin Jihar Kano don kai gaisuwar ta’aziyya ga Gwamna Bala Muhammed.
Gwamnan Bauchi ya rasa abokiyar zaman mahaifiyarsa a baya-bayan nan.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce; “Marigayiyar ta kasance mace mai kirki da jajircewa, kuma ba za a manta gudunmawarta ga iyalanta da al’umma ba.”
“Muna roƙon Allah Madaukakin Sarki ya gafarta mata, ya sanyata a Aljanna Firdausi, kuma ya bai wa iyalanta ƙarfin hali don jure wannan babban rashi.”