Gamayyar Kungiyoyin Arewa ta bayyana rashin jin dadinta kan matsayar gwamna Rotimi Akeredolu a kan kin amincewa da ‘yan takara daga yankin Arewa a zaben 2023.
A cewar kungiyar, lallai gwamnan na Ondo ya yi magana ne a matsayinsa na cikakken wanda a ayyana kansa a matsayin makiyin Arewa da dimokuradiyya.
Har ila yau, kungiyar ta lura cewa, Arewa ba za ta bari wasu daga Kudancin kasar nan su razana su ba, wadanda ke barazana a kullum da zage-zage, da kuma yada kiyayya.
Kalaman Gwamna Rotimi Akeredolu na cewa duk jam’iyyar siyasar da ta tsayar da ‘yan takara daga yankin Arewa gabanin zaben 2023, za ta riga rana faduwa, wanda ya jawo masa mummunan bakin jini tare da martani daga Arewacin kasar nan.