fidelitybank

Gwagwarmayar sabon sakataren Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya naɗa Umar Farouk Ibrahim a matsayin sabon sakataren gwamnatin jihar.

Cikin wata sanarwa da Sakataren yaɗa labaran gwamnan, Sanusi Barure Dawakin Tofa ya fitar, ya ce gwamnan ya zaɓi Umar Ibrahim ne bisa ƙwarewar da yake da ita a fagen aikin gwamnati.

Gwamnan ya ce yana fatan sabon sakataren gwamnatin zai taimaka wajen inganta harkokin gwamnatin jihar.

“Muna sa ran zai taka muhimmiyar rawa wajen ciyar da gwamnatin jihar gaba, don cimma manufofin da ta sa a gaba”, in ji sanarwar.

A watan Disambar shekarar da ta gabata ne Gwamna Abba ya sauke tsohon sakataren gwamnatin jihar, a wani garambawul da ya yi wa majalisar zartarwarsa.

Naɗin sabon sakataren zai soma aiki ne daga gobe Litinin 10 ga watan Fabrairu, a cewar sanarwar.

Wane ne sabon sakataren gwamnatin?

Umar Farouk Ibrahim ya samu digirinsa na farko a fannin kimiyyar siyasa a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya a shekarar 1985.

Ya fara aiki a shekarar 1987 zuwa 2023 lokacin da ya yi ritaya bayan shafe fiye da shekara 30 yana aiki, kuma ya riƙe manyan muƙamai ɓangarori daban-daban a fadin jihar, ciki har da babban sakataren dindindin a ofishin sakataren gwamnatin jihar daga 2001 zuwa 2015.

Haka kuma ya riƙe irin wannan muƙamin a ma’aikatar ayyukan gwamnatin jihar daga 2015 zuwa 2016.

Ya kuma riƙe muƙamin sakataren gwamnatin jihar na riƙo har sau biyu a 2013 da 2014 a lokacin da sakataren gwamnatin na wancan lokacin ya tafi hutu.

Ya kuma kasance cikin manyan kwamitocin gwamnati daban-daban.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp