Majalisar wakilai ta bukaci kamfanin man fetur na kasa (NNPC) da ya dakatar da kamfanonin da ke da hannu, wajen shigo da man fetur da aka gurbata da sinadarin Methanol.
Majalisar ta kuma bukaci NNPC da ta mika sunayen kamfanonin ga kwamitin ta, domin gudanar da cikakken bincike.
The Cable ta rawaito cewa, an zartas da hakan ne yayin zaman majalissar da aka yi a ranar Alhamis 10 ga watan Fabarairu, bayan amincewa da kudirin da Mohammed Monguno ya dauki nauyinta.
Mele Kyari, Manajan Darakta na Kamfanin NNPC, ya ce, MRS, Oando, Emadeb Consortium, da Duke Oil, wani reshen NNPC ne suka shigo da man da aka gurbata da methanol a wannan karon.