fidelitybank

Guguwa ta kashe mutane uku a Taraba da Nassarawa

Date:

Rahotanni na cewa a kalla mutane uku ne suka rasa rayukansu a garin Takum da ke jihar Taraba sakamakon wata guguwa da ta faru sau biyu cikin kwana biyu.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito wani mazaunin garin Mallam Maiwada Takum na cewa, guguwar ta soma faruwa ne da yammacin ranar Talata inda ta yi gagarumar ɓarna ga gidaje da makarantu da ofisoshi.

Takum ya ƙara da cewa da farko an yi mamakon ruwan sama daga bisani kuma aka yi guguwa mai ƙarfi da ta shafe fiye da sa’a ɗaya da rabi tana zagawa.

Shi ma wani mazaunin garin, Yakubu Adamu, ya bayyana cewa guguwar ta yi matuƙar ɓarna inda ta salwantar da gidaje da rayuka.

Babban mai bai wa gwamnan jihar shawara kan yaɗa labarai, Emmanuel Bello ya ce gwamna Agbu Kefas ya higa garin domin duba irin ɓarnar da guguwar ta yi.

An kuma bayar da rahoton mutuwar mutum ɗaya da jikkatar wasu da dama sakamakon tashin guguwa da ta lalata gidaje fiye da 100 a yankin Agbashi da ke ƙaramar hukumar Doma a jihar Nassarawa.

Mataimakin shugaban ƙaramar hukumar, John Bako-Ari ne ya tabbatar da lamarin inda ya ce guguwar ta tashi ne ranar Talata da yamma.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp