Shirye-shiryen mayar da fom ɗin takarar tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonatha,n a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na ci gaba da yin nisa.
Wannan dai ya zo ne kamar yadda kungiyar Fulanin da ta sayi fom ɗin takarar shugaban kasa na Naira miliyan 100 na APC da kuma nuna sha’awarta ga Jonathan a ranar Alhamis, ta ce, za ta mika fom din a ranar Juma’a, kamar yadda jaridar The PUNCH ta ruwaito.
Ku tuna cewa, Jonathan ya ki amincewa da fom din tsayawa takarar jam’iyyar da hadin gwiwar makiyayan Arewa suka saya masa.
A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ikechukwu Eze ya fitar, tsohon shugaban ya ce, ba shi da alaka da kungiyar Fulani da ta ce, ta sayi fom din shugaban kasa da sunan sa.
Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon shugaban kasar ya koma jam’iyya mai mulki, kuma yana son tsayawa takarar shugaban kasa idan har aka cika wasu sharudda.