Shahararren dan gwagwarmayar nan na Najeriya, Deji Adeyanju ya yi ikirarin cewa, tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a 2023 zai tafi yankin Kudu maso Kudu.
Adeyanju ya yi wannan ikirarin ne a ranar Alhamis a shafinsa na Twitter Tare da hoton Rotimi Amaechi da Godwin Emefiele, Adeyanju ya ce, jam’iyyar APC na tunanin baiwa wani dan kabilar Igbo tikitin takarar shugaban kasa.
Adeyanju ya yi ikirarin cewa, wata majiya a jam’iyyar APC ta shaida masa cewa, za a hana Asiwaju Tinubu da Yemi Osinbajo tikitin takarar shugaban kasa a 2023.
Ya kara da cewa: “Da alama tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC zai je Kudu-maso-Kudu kuma fa’idar da dukkan su ke da ita ita ce, an dauke su ‘yan kabilar Igbo ne.
“Kudu maso Yamma ba za su samu ba a cewar majiyoyi da dama a APC. In ji shi.
Adeyanju ya kara da cewa, tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya na da damar samun tikitin takarar shugaban kasa fiye da Tinubu.