Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya saki wata takarda wacce za ta iya janyo cece-kuce cikin manyan ‘yan siyasar kasar nan.
A cewar Jonathan, ya na da yakinin dan takarar shugaban kasa, Gwamna Bala Mohammed zai iya shugabantar Najeriya ba tare da samun tangarda ba.
Tsohon shugaban kasar ya kwatanta Bala, wanda ya rike kujerar ministan Abuja a lokacin ya na shugaban kasa, a matsayin mutum jajirtacce, kuma tsayayye.
Talabijin na Channeks ya rawaito cewa, Goodluck Ebele Jonathan ya bayyana yakinin sa akan Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi dangane da mulkin kasar nan a 2023.