fidelitybank

Gombe: ‘Yar Majalisar dokoki ta sauya sheka daga PDP zuwa APC

Date:

Mace daya tilo a majalisar dokokin jihar Gombe, Honourable Asma’u Mohammed Iganus ta jam’iyyar PDP ta jagoranci magoya bayanta wajen ficewa daga jam’iyyar zuwa jam’iyyar APC.

Da ya ke karbar Asma’u Iganus mai wakiltar mazabar Jihar Shongon da Magoya bayanta na jam’iyyar PDP a APC, Gwamna Inuwa ya tabbatar wa ‘yar majalisar a shirye ya ke ya yi mata aiki, domin ganin jam’iyyar APC ta samu nasara a 2023 da ma gaba.

An gudanar da liyafar karbar ‘yar majalisar ne a Lapan, karamar hukumar Shongom inda Gwamna Inuwa shi ma ya nuna jin dadinsa da karbar ta da magoya bayanta.

Ya yaba da hazakar siyasar Hon. Asma’u Iganus ta ce ta koma jam’iyyar APC ba bisa katsa landan ba, amma zabin da na yi ya yi nuni da irin rawar da jam’iyyar ke takawa a jihar.

Gwamnan ya ce, “Tun kafin ta yanke shawarar komawa jam’iyyar APC, ta taba zuwa wurina ta gabatar da koke a kan bukatar sake gina gada a mazabarta kuma na biya mata bukatunta, kuma na yi aikin ba tare da wata tangarda ba”.

A cewar Gwamnan, gwamnatin APC a jihar Gombe ta himmatu wajen aiwatar da manufofi da shirye-shirye masu tasiri kai tsaye ga rayuwar al’ummar jihar.

Ya ce,”Shigowar Asma’u da magoya bayanta sama da 2000 ba zai iya zuwa ba a daidai lokacin da gwamnatin APC a jihar ke samar da yanayi mai dorewa na zamantakewa da tattalin arziki da samar da ababen more rayuwa da za su kasance a cikin al’umma, dadewa ya samar da ayyukan yi ga dimbin matasan jihar”.

Ya bayyana cewa aiwatar da shirin gina titin ‘Network 11-100’ ya na ci gaba da tafiya kamar yadda a ka bayyana a cikin takardar manufofin gwamnatinsa tare da tabbatar wa al’ummar Karamar Hukumar Shongom cewa nan ba da jimawa ba za a fara hanyoyin da su ka hada Filiya zuwa Gundali da Lapan zuwa Burak.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...
X whatsapp