fidelitybank

Gombe: ‘Yar Majalisar dokoki ta sauya sheka daga PDP zuwa APC

Date:

Mace daya tilo a majalisar dokokin jihar Gombe, Honourable Asma’u Mohammed Iganus ta jam’iyyar PDP ta jagoranci magoya bayanta wajen ficewa daga jam’iyyar zuwa jam’iyyar APC.

Da ya ke karbar Asma’u Iganus mai wakiltar mazabar Jihar Shongon da Magoya bayanta na jam’iyyar PDP a APC, Gwamna Inuwa ya tabbatar wa ‘yar majalisar a shirye ya ke ya yi mata aiki, domin ganin jam’iyyar APC ta samu nasara a 2023 da ma gaba.

An gudanar da liyafar karbar ‘yar majalisar ne a Lapan, karamar hukumar Shongom inda Gwamna Inuwa shi ma ya nuna jin dadinsa da karbar ta da magoya bayanta.

Ya yaba da hazakar siyasar Hon. Asma’u Iganus ta ce ta koma jam’iyyar APC ba bisa katsa landan ba, amma zabin da na yi ya yi nuni da irin rawar da jam’iyyar ke takawa a jihar.

Gwamnan ya ce, “Tun kafin ta yanke shawarar komawa jam’iyyar APC, ta taba zuwa wurina ta gabatar da koke a kan bukatar sake gina gada a mazabarta kuma na biya mata bukatunta, kuma na yi aikin ba tare da wata tangarda ba”.

A cewar Gwamnan, gwamnatin APC a jihar Gombe ta himmatu wajen aiwatar da manufofi da shirye-shirye masu tasiri kai tsaye ga rayuwar al’ummar jihar.

Ya ce,”Shigowar Asma’u da magoya bayanta sama da 2000 ba zai iya zuwa ba a daidai lokacin da gwamnatin APC a jihar ke samar da yanayi mai dorewa na zamantakewa da tattalin arziki da samar da ababen more rayuwa da za su kasance a cikin al’umma, dadewa ya samar da ayyukan yi ga dimbin matasan jihar”.

Ya bayyana cewa aiwatar da shirin gina titin ‘Network 11-100’ ya na ci gaba da tafiya kamar yadda a ka bayyana a cikin takardar manufofin gwamnatinsa tare da tabbatar wa al’ummar Karamar Hukumar Shongom cewa nan ba da jimawa ba za a fara hanyoyin da su ka hada Filiya zuwa Gundali da Lapan zuwa Burak.

nigeria peace corps

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp