fidelitybank

Gobe ne Abba da Gawuna za su san makomarsu a kotun daukaka

Date:

Kotun daukaka kara ta sanya Juma’a, 17 ga watan Nuwamba, a matsayin ranar yanke hukunci kan karar da gwamnan Kano ya daukaka, inda yake kalubalantar soke nasarar zabensa.

Abba Kabir Yusuf ya garzaya gaban kotun daukaka kara, bayan kotun korafin zabe ta jihar Kano a ranar 20 ga watan Satumba, ta rushe nasarar da ya samu, inda ta ce abokin takararsa na jam’iyyar APC Nasir Yusuf Gawuna ne halastaccen wanda ya ci zabe.

Kotun dai ta kafa hujjar hukuncin da ta yanke ne a kan kuri’u sama da 165,000 da ta soke daga cikin abin da Abba Kabir Yusuf na NNPP ya samu, saboda rashin sa hannu da kwanan wata da kuma hatimin hukumar zabe. Jam’iyyar APC, ita kuwa ta roki kotun ta yi watsi da karar da Gwamna Abba Kabir ya daukaka.

Hukuncin kotun daukaka karar na zuwa ne kwana goma cif bayan alkalan kotun da ke zama a Abuja, sun saurari bahasin dukkan bangarorin da ke cikin shari’ar, tare da sanya hukuncinsu a mala, sannan suka ce za su sanar da ranar yanke hukunci nan gaba.

Wata takardar kotun daukaka kara da BBC ta gani, ta lissafa APC da NNPP da kuma INEC a matsayin wadanda ake kara. Sannan ta ce kotun za ta fara zaman yanke hukunci daga misalin karfe 9:00 na safe.

Shari’ar zaben gwamnan Kano na daya daga cikin shari’o’in zabe mafi muhimmanci tun bayan kada kuri’a a babban zaben kasar cikin watan Fabrairu da Maris.

Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya tana fatan kotu za ta dawo mata da kujerar gwamna, wadda ta kubuce daga hannunta, zuwa hannun jam’iyyar adawa ta NNPP, yayin da NNPP ke alla-alla ta tsira da kujerar gwamna daya tilo da ta samu bayan zaben 2023.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp