fidelitybank

Gobarar California ta laƙume rayukan Mutane 10

Date:

Jami’ai a birnin Los Angeles sun ce mummunar gobarar daji ta lalata sama da gidaje dubu 10 da wasu gine-gine a jihar Californian Amurka.

Kawo yanzu adadin waɗanda aka tabbatar da mutuwarsu ya kai 7, ana kuma ci gaba da neman wasu.

Brad Sherman ɗan majalisa ne mai wakiltar Carlifornia, ya bayyana halin da ake ciki, inda ya ce wannan ce gobara mafi muni a tarihin Amurka.

Ya ce babu wanda ya taɓa tsammanin lamarin zai kai haka ga kuma iska mai ƙarfin da ake fama da ita na ƙara rura wutar.

Ƙiyasin ɓarnar da wutar dajin ta yi ya tashi sosai zuwa aƙalla dala miliyan 135.

An tura jami’an tsaro na ƙasa 400 a yankin domin taimaka wa ƴansanda aikin, bayan da aka samu rahotanni sata ko kwashe kayan jama’a. In ji BBC.

Da yake magana a wani taron manema labarai , babban jami’in ƴansanda na birnin na Los Angeles, Jim McDonnell, ya ce abin da suka mayar da hankali yanzu a kansa shi ne kare aikata miyagun laifuka.

Ya ce, “kare gidaje da harkokin kasuwanci a wuraren da aka kwashe jama’a da inda babu tsaro sosai shi ne abin da muka bayar da fifiko a kai yanzu, domin tabbatar da ganin cewa babu wanda ya yi amfani da damar mawuyacin halin da ake ciki. Ko kaɗan ba za a lamunta wawashe kayan jama’a ba ko wawason kaya ko ribatar wannan bala’i.”

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp