Jami’an lafiya a birnin Los Angeles na Amurka sun ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon gobarar da ke ci gaba da ruruwa a yankin ya kai 16.
Ma’aikatan lafiyar sun kuma yi gargaɗin cewa adadin ka iya zarta haka, yayin da wutar da ci gaba.
Jirage masu saukar ungulu da marasa matuƙa dai na ta ƙoƙarin kashe gobarar wadda ta tashin tun a ranar Talata.
Tuni hukumomi suka bayar da umarnin kwashe ƙarin mutane yayin da suke fargabar gobarar za ta isa Brentwood, ɗaya daga cikin wuraren mafiya muhimmanci a birnin.