Wata gobara ta tashi a kasuwar Karimo da ke Abuja, babban birnin tarayya Abuja.
Duk da cewa har yanzu ba a san ainihin musabbabin tashin gobarar ba, wasu ‘yan kasuwar sun ce, ya taso ne daga wani shago kafin ta bazu ga sauran.
Jaridar Politics Nigeria ta fahimci cewa, wannan ne karo na hudu da kasuwar Karimo da wuta ta kama.
Har zuwa lokacin nan ba a san irirn asarar da wutar ta ba. Ana kyautata zaton gobarar ta lalata kayayyaki na miliyoyin Naira.
Rahotanni daga kafafen yada labarai sun nuna cewa, a tsakanin shekarar 2019 zuwa 2021, Najeriya ta fuskanci mummunar gobara, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 79 daga cikin gobara 68 da aka samu cikin watanni 18.
Har ila yau, kididdiga daga Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya (FFS) ta nuna cewa, tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021, an yi wa hukumar kiraye-kiraye 4,541 a duk fadin kasar kuma an yi rikodin gaggawar ceto 378.