Gobara ta tashi a hawa na biyu na hedikwatar tsaro da ke Abuja.
Har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar da ta faru a ranar Litinin ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.
Daraktan yada labarai na tsaro, Manjo Janar Jimmy Akpor, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin ya bayyana cewa an shawo kan lamarin.
Ya ce an shawo kan lamarin ne sakamakon hadin gwiwa da sojoji da jami’an hukumar kashe gobara ta tarayya suka yi.
An kuma kwashe dukkan ma’aikata da ma’aikatan farar hula ba tare da jikkata ko asarar rai ba.
“Haka zalika, al’amuran yau da kullum sun dawo. An fara bincike don gano musabbabin tashin gobarar.
“Muna godiya ga hukumar kashe gobara ta tarayya da sauran jama’a saboda ci gaba da goyon baya da fatan alheri ga rundunar sojojin Najeriya,” inji shi.