Akalla daruruwan mutane ne ake fargabar sun mutu, sakamakon gobara da ta kama wani haramtacciyar matatar danyen mai a dajin Abaezi da ke karamar hukumar Ohaji-Egbema a jihar Imo.
DAILY POST ta rawaito cewa, wasu kimanin dari da hamsin sun sami munanan raunuka na konewa.
Da yake tofa albarkacin bakinsa, kwamishinan albarkatun man fetur na jihar, Goodluck Opiah, wanda ya wakilci gwamna Hope Uzidinma na jihar Imo a ziyarar da ya kai wurin, ya ce gobarar ta lakume rayukan matasa da dama.
Ya ce, “a halin yanzu, ba zan iya tabbatar da adadin wadanda suka mutu ba, saboda da yawa daga cikin ‘yan uwa sun kwashe gawarwakin wasu da dama.“
Opiah ya bayyana cewa, gwamnatin jihar Imo ta bayyana cewa, tana neman Okenze Onyewoke wanda ya mallaki matatar man ba bisa ka’ida ba.