Hukumar kashe gobara a jihar Kaduna, ta ce, mutum shida ne suka mutu a gobara 114 da aka yi a jihar a yankuna uku kacal.
Jaridar The Nation, ta rawaito cewa, daraktan hukumar, Paul Aboi, ya bayyana hakan a wata zantawa da ya yi da manema labarai a Kaduna.
Ya ce, an samu gobarar ne a yankunan Kaduna da Zaria da kuma Kafanchan.
Aboi ya ce,”Hukumar mu ta ceto mutane hudu wadanda ba su jikkata ba, yayin da mutum 8 suka jikkata sakamakon gobarar.
“Hukumar ta ceto dukiyar da ta kai darajar biliyan 4,3 yayin da dukiyar da aka yi asara ta kai darajar miliyan 785 a cikin wata guda, in ji shi.