Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, ta ce, ta ceci rayuka da dukiyoyi 135 da kudinsu ya kai Naira miliyan 34.6 daga aukuwar gobara 42 a watan Yuni.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na hukumar Alhaji Saminu Abdullahi a Kano.
Abdullahi ya ce, mutane 24 ne suka mutu, sannan an kiyasta asarar dukiya ta Naira miliyan 13 da gobarar ta yi a lokacin.
A cewar sa, ma’aikatar ta amsa kiraye-kirayen ceto 77 da kuma kararrawar karya 17 daga mazauna jihar.Kakakin ya danganta gobarar da rashin kula da amfani da na’urorin lantarki marasa inganci.
Ya shawarci jama’a da su rika kula da gobarar a hankali don gujewa tashin gobara, yayin da bukukuwan Sallah ke gabatowa.
Abdullahi ya kuma bukace su da su rika bin dokokin hanya domin gujewa hadurran mota yayin bikin.