Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta ce, gobara ta kone shaguna 37 a unguwar Zawaciki da ke karamar hukumar Kumbotso a jihar Kano.
Kakakin hukumar, Alhaji Saminu Abdullahi ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN cewa gobarar ta faru ne da misalin karfe 01:37 na safiyar Laraba.
A cewar Abdullahi, da misalin karfe 01:37 na safe ne muka samu kiran wani Malam Baba cewa an samu tashin gobara a Zuwaciki.
“Mun yi gaggawar tattara jami’an mu zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 01:47 na safe, muka kashe gobarar domin kada ta bazu zuwa wasu shaguna,” inji shi.
Abdullahi ya ce shagunan 37 sun kasance a kasan bene na wani gini mai amfani da yawa.
Ya kuma kara da cewa gobarar ta dan yi barna a wasu shaguna uku.
A cewarsa, ba a samu asarar rai ba, kuma ana kan binciken musabbabin tashin gobarar.