fidelitybank

Gobara ta kona shaguna 18 a jihar Sokoto

Date:

Wata gobara da ta tashi a babbar kasuwar jihar Sokoto da safiyar yau Litinin ta yi sanadin ƙonewar shaguna da dama a ɓangaren masu sayar da babura da kekuna.

Garba Muhammad Gwazi, shugaban ƴan mashin reshen jihar ya shaida wa BBC cewa gobarar ta laƙume shaguna ‘180’ na masu sayar da mashin.

A cewarsa, har yanzu ba a san abin da ya janyo tashin gobarar ba da ta janyo asarar dukiya ta miliyoyin naira. Sai dai ya ce gobarar ta soma ne daga wata shara da aka tara.

Ya bayyana cewa gobarar ba ta kai ga asarar rai ko jikkata ba.

Gwazi ya kuma yi kira ga gwamnati ta kai masu ɗauki domin “kasuwancinmu ya miƙe ya ci gaba.” in ji shi.

Shi ma Honarabul Ibrahim Muhammad Giɗaɗo, mai bai wa gwamna shawara kan babbar kasuwar ya ce wutar ta tashi da sanyin safiyar yau.

Ya ce “ɓangaren da ya ƙone sosai a cikin kasuwar shi ne na ƴan mashin da kekuna, ana iya samun shago guda ɗauke da mashin fiye da 200 ko 100, shagunan gaba ɗaya sun ƙone,”

“Waɗannan mashina akwai waɗanda suka haura miliyan, akwai asara mai yawa.” ya ƙara da cewa.

Giɗaɗo ya ƙara da cewa jami’an kashe gobara sun kashe kashi 80 cikin 100 na gobarar da ke ci. In ji BBC.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp