Wata gobara ta lalata shaguna da dama a babbar kasuwar Gusau da ke jihar Zamfara inda kuma ta kashe mutum daya.
Rahotanni sun ce gobarar ta tashi ne da misalin karfe tara, na daren ranar Litinin a bangaren kayan ɗaki na babbar kasuwar.
Kwamandan hukumar kashe gobara ta Najeriya, Hamza Mohammed, ya sanar da gidan talabijin na Channels cewa wani mai shago wanda har yanzu ba a bayyana sunansa ba ya mutu a lokacin da yake kokarin shiga shagonsa domin kashe gobarar.
Jami’an kashe gobara daga rundunar ‘yan sandan jihar sun yi ta fama da gobarar tun karfe tara na dare. domin hana yaduwar ta zuwa wasu shaguna.