Gobara ta kone daya daga cikin ofisoshin hukumar zabe ta kasa (INEC) a jihar Zamfara.
Wurin da abin ya shafa dai ofishin alkalan zabe ne da ke karamar hukumar Kaura Namoda a jihar, inji mazauna yankin.
Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara da hukumomin INEC a jihar ba su tabbatar da faruwar lamarin ba, ko kuma an samu asarar rayuka, har zuwa lokacin hada wannan rahoto. A cewar Talabijin ɗin Channels.
Duk ƙoƙarin jin ta bakin Shugaban Ilimi da Yada Labarai na INEC a Jihar Zamfara, yunkurin yin hakan ya ci tura.