fidelitybank

Gobara ta kama a kasuwar Potiskum

Date:

Gobara ta kone wasu sassan wata shahararriyar kasuwar Potiskum a jihar Yobe.

An ce gobarar ta tashi ne a ranar Lahadi da misalin karfe 8 na dare.

Duk da cewa ba a samu asarar rai ba, gobarar ta lalata kadarori na miliyoyin Naira a sassan kasuwar kayan sawa da doya da keke da kuma shagunan sayar da kayayyaki (POS) na kasuwar.

Kawo yanzu dai ba a gano ainihin musabbabin faruwar lamarin ba, har zuwa lokacin da aka gabatar da wannan rahoto, domin an ce kasuwar ba ta da wutar lantarki a lokacin da lamarin ya faru.

An tattaro cewa Samariyawa nagari ne suka kashe gobarar sakamakon rashin mayar da martani daga hukumar kashe gobara da ke Potiskum da kuma tashoshin da ke makwabtaka da ita.

Jami’an Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA), da sanyin safiyar yau sun ziyarci wurin domin jajantawa da kuma tantance irin barnar da aka yi da nufin bayar da agajin da ya dace ga wadanda bala’in ya shafa.

Rikicin gobara dai ya kasance wani lamari ne da ke ci gaba da faruwa a kasuwar, lamarin da ya janyo asarar dukiya mai yawa.

leadership news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naÉ—in...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa Æ´an wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...

Yan Bindiga sun yi wa Mutane 38 yankan Rago a Zamfara

Ƴanbindiga sun kashe wasu mutum 38 ta hanyar yi...
X whatsapp