fidelitybank

Gobara ta ci wani sashe a kasuwar Ƴan Katako a Legas

Date:

Gobara ta lakume kasuwar katako da ke kan hanyar Pipeline Street a yankin Ikotun na Jihar Legas a ranar Alhamis, inda ta lalata wani ɓangare na kasuwar.

A cewar wata sanarwa da Babban sakatare na hukumar ba da aagajin gaggawa ta jihar Legas (LASEMA), Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya fitar, gobarar ta shafi shaguna huɗu kacal.

Ya ce, saurin amsa kiran agajin hukumar daga Igando, tare da haɗin kai da sauran ma’aikatan da suka isa wurin, sun hana wutar bazuwa zuwa gine-ginen da ke makwabtaka da wurin.

Babban Sakatare na LASEMA ya lura cewa binciken farko bai gano musabbabin gobarar ba har zuwa lokacin da aka bayar da wannan rahoto.

Ya kuma bayyana cewa babu asarar rayuka ko rauni da aka samu sakamakon wannan gobarar.

Wannan yana zuwa ne bayan wani rahoto na tashin gobara a ofishin hukumar bincike kan nasana’antu ta kasa (FIIRO) da ke Oshodi a safiyar ranar.

LASEMA ta tabbatar da cewa gobarar ta tashi sakamakon yawan amfani da janareta da ya yi zafi.

Ita ma wannan gobarar an shawo kanta, babu asarar rayuka ko raunuka da aka samu sakamakon lamarin.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp