Wasu Giwaye sun kashe mutum biyar a wani farmaki da suka kai wa manoma yayin da suke girbin amfanin gonarsu a wani kauye da ke gundumar Macomia a Arewacin lardin Cabo Delgado a Mozambique.
Wasu daga cikin wadanda suka gudu a lokacin da giwayen suka kai harin, bayan sun koma ne suka ga gawawwakin ‘yan uwansu da giwayen suka tattake.
Bayanai sun nuna cewa mutanen a da ‘yan gudun hijira ne wadanda ba su dade da komawa kauyen nasu ba.
Lardin Cabo Delgado, wuri ne da yake fama da matsalar mayaka masu ikirarin jihadi tun 2017, abin da ya tilasta wa dubban mutane tserewa daga gidajensu. In ji BBC.
Gundumar Macomia tana makwabtaka da gandun-daji na Quirimbas na kasa, wanda tsawon shekaru ba a samu irin wannan hari na giwaye ba, har ma a lokacin da masu da’awar jihadi ke kai hare-hare.