A yayin da aka yi kiran sallah a birnin Sagaing a ranar Juma’ar da ta gabata, ɗaruruwan Musulmai ne suka gaggauta zuwa masallatai biyar da ke birnin da ke tsakiyar Myanmar.
Sun tafi domin yin sallar Juma’ar ƙarshe a watan Ramalana, ƴan kwanaki gabannin bikin sallar idi.
Sai dai ƙarfe 12:51 agogon ƙasar, sai aka samu girgizar ƙasa. masallatai uku suka rushe, cikinsu har da mafi girma na Myoma, kuma kusan dukanin mutanen da ke ciki suka mutu.
Can wasu ɗaruruwan kilomita a masallacin Soe Nay Oo da ke garin da ke bakin iyakar Thailand na Mae Sot, shi ma girgizar ƙasar ta shafe shi.
Kwana ɗaya bayan girgizar ƙasar ne tsohon limamin masallacin Myoma ya gano cewa kimanin mutane 170 ciki har da ƴan uwansa da abokai da masu binsa sallah a baya, duka sun mutu a cikin masallacin.
Wasu daga cikinsu ƙusoshi ne a ƙungiyar al’ummar musulmi.
Fiye da mutane 2,700 ne suka mutu a girgizar ƙasar da ta auku a kusa da Sagaing da Mandalay, birni na biyu mafi girma a Myanmar.
Adadin waɗanda suka mutu a girgizar ƙasar na ƙaruwa, yayin da ake ci gaba da tono gawawwaki daga ƙarƙashin baraguzai.