fidelitybank

Girgizar Kasa: ‘Yan Turkiyya sun bukaci agajin ‘yan Najeriya

Date:

Ofishin jakadancin Turkiyya da ke Abuja da kuma kungiyar kare ‘yancin Musulmi ta Najeriya wato MURIC a takaice sun bukaci da a taimaka wa wadanda bala’in girgizar kasa ya afka wa a Turkiyya da Syria.

A sanarwar neman taimakon da ofishin jakadancin ya fitar jiya Lahadi a Abuja, ya bayyana irin kayayyakin da ake matukar bukata, wadanda suka hada da tufafi na sanyi da takalma da wanduna da safar hannu da safa da makamantansu.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ana kuma bukatar tantuna da gadaje da katifu da barguna da fulas da cocilan da jannareto da sauransu.

Karanta Wannan: Girgizar Kasa: An kama mutane 12 a cikin ‘yan kwangilar gini 13 a Turkiyya

Harwayau, sanarwar ta bayyana irin bkayan abincin da ake bukata da suka kunshi abincin gwangwani da abincin jarirai na gwangwani da audugar kunzugu ta yara da ta mata da sauran kayayyakin bukata na tsaftar jiki da muhalli.

A ranar 6 ga watan Fabarairu ne girgizar kasa mai karfin gaske ta fada wa kasashen Turkiyya da Syria inda ta yi sanadin mutuwar mutane sama da dubu 30, tare da jikkata dubbai da lalata gidaje da kayayyaki.

A sanarwar an bayyana wuraren da za a kai kayan taimakon a Abuja lamba 46 Aminu Kano Crescent Wuse 2 sai da Lagos ARMADA International Limited 8 Solomon Agbontan Road (Aerodrome Road) Apapa.

Ita ma a sanarwar da ta fitar kungiyar kare muradun Musulmi ta Najeriya MURIC, kamar yadda Babban Darektanta Farfesa Ishaq Akintola, ya bukata, ta yi kira ga masu hali a Najeriya da su bayar da taimakon domin tallafa wa wadanda bala’in ya fada wa.

legitnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp