fidelitybank

Girgizar Kasa: Sama da mutane 28,000 sun mutu a Syria da Turkiyya

Date:

Adadin mutanen da suka mutu sakamakon bala’in girgizar ƙasar da ya afka wa ƙasashen Turkiyya da Siriya ya zarta 28,000, yayin da ake ci gaba da aikin ceto.

To sai dai fatan samun ƙarin masu numfashi na gamuwa da cikas yayin da ake samun rahotonnin rashin zaman lafiya a wasu yankunan kudancin Turkiyya, lamarin da ke yin barazana ga masu aikin ceton kamar yadda wasu ƙungiyoyin agaji uku suka bayyana..

Ƙungiyar agaji ta ƙasar Jamus da takwararta ta ƙasar Austria sun dakatar da ayyukansu ranar Asabar, sakamakon abin da suka kira rikici tsakanin wasu ƙungiyoyi a yankin.

Wani jami’in ceto ya ce ana fargabar ƙaruwar tabarɓarewar tsaro, yayin da jigilar kayan abinci zuwa yankin ke gamuwa da cikas.

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya ce zai yi amfani da ƙarfi wajen ladabtar da duk wanda yake ƙoƙarin karya doka.

Aƙalla gidaje 6,000 ne suka rushe a Turkiyya, lamarin da ke ɗiga ayar tambaya game gwamnatin Recep Tayyip Erdogan za ta iya yin abin da ya kamata domin kare rayuka.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana girgizar ƙasar da ‘mummunan bala’in’ da yankin ya taɓa gani cikin shekarar 100.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp