Jami’an Turkiyya, sun ce, sun bayar da izinin kama mutum 113 saboda hannu a aikin gine-ginen da suka rufta a lokacin girgizar ƙasar da ta afku ranar Litinin.
‘Yan sandan ƙasar sun kama akalla mutum 12, ciki har da masu kwangilar gine-ginen.
Tashe-tashen hankula na kawo tsaiko ga aikin ceton a wasu sassan kudancin Turkiyya,
Adadin waɗanda aka tabbatar da mutuwarsu a Turkiyya da Siriya ya zarta 30,000.
Ana sa ran samun ƙarin mutanen da za a kama a ƙasar, lamarin da ake ganin tamkar ɗora alhakin bala’in kan wasu mutane daban.
Masana sun kwashe shekaru suna gargaɗin cewa sabbin gine-gine a ƙasar suna cikin hatsari sakamakon wasu tsare-tsaren gwamnati da ke kunshe da rashawa a cikinsu. A cewar BBC.
Waɗannan tsare-tsare suna yi wa ‘yan kwangila afuwa waɗanda a wasu lokuta ke yi wa dokokin gine-ginen ƙasar karan-tseye, a ƙoƙarinsu na haɓaka gine-gine, ciki har da yankunan da ke da hatsarin samun girgizar ƙasa.
Dubban gine-gine ne dai suka rushe a lokacin girgizar ƙasar da ta afku a ƙasar, lamarin da ya sa ake ɗiga ayar tamabaya game da cewa ko rashin bin ƙa’idar gine-gine ce ta haddasa munana bala’ain.